in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sace wasu 'yan kasashen waje a arewacin Najeriya
2018-01-18 15:40:55 cri
Rahotanni daga Najeriya na cewa, wasu 'yan bindiga sun yi garkuwa da wasu Amurkawa guda biyu da 'yan Kanada guda biyu a jihar Kadunan Najeriya.

'Rundunar 'yan sandan Kaduna ta ce, da misalin karfe bakwai na daren ranar Talata ne, wasu 'yan bindigan da ba'a san ko su wane ne ba suka yi wadannan mutane hudu kwanton bauna a kan hanyarsu daga Kaduna zuwa birnin Abuja, lamarin da ya kai ga kisan 'yan sanda biyu dake yi musu rakiya.

A halin yanzu 'yan sanda na kokarin kubutar da 'yan kasashen wajen da aka yi garkuwa da su.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China