in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta tsananta tsaro a jihar Rivers mai arzikin man fetur
2018-01-05 10:43:56 cri
Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta tura karin jami'an yaki da kungiyoyin asiri da na yaki da satar mutane da ta'addanci, zuwa yankin Omoku na jihar Rivers mai arzikin man fetur, domin zakulo wadanda suka kashe masu ibada 16 a ranar da aka shiga sabuwar shekara.

Kwamishinan 'yan sandan jihar Zaki Ahmed, ya shaidawa manema labarai a birnin Fatakwal cewa, an kara baza jami'an tsaro a yankin na Omoku domin tabbatar da tsaro da kuma farautar wadanda ake zargi.

Da sanyin safiyar ranar Litinin ne aka kashe wasu mutane 16 tare da jikkata wasu 12, a lokacin da suka fito daga coci bayan gudanar da addu'o'in shiga sabuwar shekara.

Zaki Ahmed ya ce 'yan sanda za su tabbatar da kama mutanen, yana mai cewa sun shiga yankin ne ta koguna cikin kwale-kwale mai amfani da inji.

Kwamishinan wanda ya ce 'yan sandan ruwa na aikin sintiri a kogunan, ya roki mazauna yankin da su taimakawa jami'an da bayanan da za su taimaka wajen cafke wadanda ake zargin.

Ya kuma ba kamfanonin kasashen waje dake aiki a yankin shawarar komawa harkokinsu ba tare da wani tsoro ba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China