in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Nijeriya ta ce dole ne a hukunta maharani jihar Benue
2018-01-05 10:25:09 cri
Gwamnatin Nijeriya ta ce dole ne a tabbatar da hukunta wadanda suka kai hari tare da yin kashe-kashe a jihar Benue dake arewa maso tsakiyar kasar.

Ministan harkokin cikin gida na kasar Abdulrahman Dambazau, ya bayyana a Makurdi babban birnin jihar Benue cewa, Gwamnati ba za ta kyale mutane su rika daukar makamai suna kai hari kan al'ummomin da ba za su iya kare kawunansu ba, sannan kuma su tsere ba tare da an hukunta su ba, ya na mai jadadda cewa za a kara kokarin ganin an zakulo masu laifin.

Abdurrahman Dambazau ya bayyana wadanda suka aikata aikin na rashin imani a matsayin bata gari, ya na mai cewa za su fuskanci fushin hukuma.

Ya kuma yi wa iyalan da suka yi rashin 'yan uwansu yayin harin ta'aziyya

A ranar 1 ga wannan wata ne wasu 'yan bindiga da ake zargin makiyaya ne, suka kai farmaki kan al'ummomin yankunan Guma da Logo na Jihar Benue.

Haka zalika an samu rahoton wasu kashe-kashen a jihohin Kaduna da Kwara da Rivers a farkon shekarar nan. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China