in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yabawa rawar da kasar Sin ke takawa game da batun sauyin yanayi
2018-01-17 09:44:55 cri
Sakatare-janar na MDD Antonio Guterres ya yabawa rawar da kasar Sin ke takawa game da magance matsalar sauyin yanayi a duniya, kana yana karfafawa kasar gwiwa wajen ci gaba da nacewa kan manufarta don ganin an cimma burin da duniya ta sanya gaba kan wannan batu.

Guterres ya fadawa 'yan jaridu cewa, suna maraba da namijin kokarin da kasar Sin ke yi wajen yaki da matsalar sauyin yanayi. Ya kara da cewa, tabbas matakan da kasar Sin din ke dauka za su yi matukar tasiri wajen samun bunkasuwar tattalin arzikinta.

Babban jami'in na MDD ya lura cewa, batun yarjejeniyar Paris da aka cimma game da sauyin yanayi ba lallai ne a iya aiwatar da ita yadda ya kamata ba, kuma batutuwan dake kunshe cikin yarjejeniyar ba za su wadatar ba wajen rage rumamar yanayin duniya a wannan karni zuwa kasa da maki biyu a ma'aunin Celsius, ko kuma kasa da maki 1.5 a ma'aunin Celsius.

Mista Guterres ya ce rawar da kasar Sin ke takawa a wannan fanni ya daga matsayin burin da ake da shi, kuma hakan ya samo asali ne sakamakon tattaunawa masu yawa da aka yi da kuma karfafa hadin gwiwa da gwamnatin kasar Sin a wannan fanni. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China