in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren MDD ya jaddada bukatar hana aukuwar tashin hankali
2017-12-21 10:51:48 cri
Babban magatakardan MDD Antonio Guterres ya jaddada muhimmancin daukar matakan hana barkewar tashin hankali,a wani mataki mai nagarta na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya.

Guterres wanda ya bayyana hakan ga zaman kwamitin sulhun majalisar, ya ce wajibi ne a hana aukuwar tashin hankali, maimakon a magance shi bayan tashin sa.

Jami'in na MDD ya kara da cewa, hana aukuwar tashin hankali zai rage kuncin da jama'a za su shiga da ma makuden kudaden da za a kashe a kokarin kwantar da wutar tashin hankalin. Ko da yake ba kowa ne zai fahimci hakan ba, amma rigakafi ya fi magani.

Ya ce, ajandar nan ta bunkasuwa nan da 2030 ta zayyana dukkan muhimman matakai da damammaki na hana aukuwar rikici. Sauran sun hada da raya kasashe, mutunta daukacin bil-Adama, inganta rayuwar jama'a da batun al'adu.

Guterres ya ce, batun daidaiton jinsi yana da alaka da jurjurcewa, an kuma samu nasara wajen damawa da mata daga batun hana tashin hankali zuwa ga batun tabbatar da zaman lafiya. Ya ce yanzu haka ,ana damawa da mata a harkokin yau da kullum. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China