in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta ce a shirye take ta tinkari mummunar barazanar tsaro da gabashin kasar ke fuskanta
2018-01-15 11:20:31 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sudan Ibrahim Ghandour ya ce, sojojin kasar sun shirya tsaf domin tinkarar mummunar barazanar tsaro da ake fuskanta a kan iyakar gabashin kasar.

Ibrahim Ghandour ya bayyana hakan ne a wajen wani taron manema labarai da ya yi tare da takwaransa na kasar Habasha Workneh Gebeyehu, wanda a yanzu haka yake ziyara a birnin Khartoum.

Ibrahim Ghandour ya ce, Sudan a shirye take ta girke sojoji don tinkarar duk wata barazana a fannin tsaro. Sa'an nan a nasa bangaren, Workneh Gebeyehu ya ce, Habasha da Sudan za su karfafa hadin-gwiwa, kana, Habasha za ta dauki matakan da suka dace domin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a wannan yanki.

Tuni a ranar 6 ga wata ne, gwamnan jihar Kassala dake gabashin kasar Sudan Adam Jamma ya sanar da rufe bakin iyakokinta da kasar Eritrea tun daga daren ranar 5 ga wata. Har wa yau, Sudan ta kara tura dakarunta zuwa wannan jiha, amma ta musunta cewa, dangantakarta da Eritrea ta yi tsami.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China