in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta sake nanata korafinta ga MDD game da iyakar Halayeb
2018-01-09 10:09:34 cri
Gwamnatin kasar Sudan ta sake nanata korafinta ga kwamitin tsaron MDD, game da takaddamar dake tsakaninta da Masar bisa yankin kan iyakar nan na Halayeb.

Ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Sudan ta fidda wata sanarwa dake tabbatar da rashin cimma matsaya tsakanin kasar da Masar, game da yankin kan iyakar nan na Halayeb, wanda a yanzu haka ke karkashin ikon Masar.

Tun daga shekarar 1958, a duk shekara Sudan na maimaita korafi ga kwamitin tsaron MDD game da yankin Halayeb, lamarin da take fatan za a warware shi, ko dai ta hanyar tattaunawa da Masar, ko kuma ta shiga tsakani na kasashen duniya.

A shekarar 2016, Masar ta yi watsi da bukatar Khartoum na hawan teburin shawarwari, ko gayyato kasashen duniya domin warware wannan takaddama. A kuma ranar Alhamis din makon jiya, Sudan ta yiwa jakadan ta dake Masar kiranye domin tattaunawa da shi. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China