in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta rufe kan iyakarta da Eritrea a hukumance
2018-01-07 12:50:22 cri
A ranar Asabar gwamnatin Sudan ta sanar da rufe kan iyakarta da kasar Eritrea ta bangaren gabashi a hukumance, bayan da Sudan din ta tura dubban dakarunta zuwa jahar Kassala wanda ke makwabtaka da Eritrea, kamar yadda kamfanin dillancin labaran kasar SUNA ya rawaito.

Gwamnan jahar Kassala Adam Jamma, shine ya bayar da umarnin rufe dukkan iyakokin kasar da Eritrea, inda ya danganta dalilan da suka sa aka rufe kan iyakar kasar da cewa an kafa dokar ta-baci ne a jahar.

Wannan mataki ya zo ne 'yan sa'o'i bayan da gwamnatin Sudan din ta musanta samun sabani tsakaninta da kasar Eritrea, ya ce an tura dakarun tsaron zuwa jahar Kassala ne saboda dokar ta-bacin da aka kafa da kuma dokar dake da nasaba da hana yaduwar makamai da ababen hawa da basu da lasisi a yankunan, kana da yakar safarar bil adama da mugaggan makamai da sauran haramtattun kayayyaki.

Dubban sojoji masu tallafawa rundunar tsaron kasar Sudan ne aka tura zuwa jahar.

A ranar 30 ga watan Disambar shekarar 2017, shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir, ya bada umarnin kafa dokar ta-baci a arewacin jahar Kordofan dake yammacin kasar Sudan da jahar Kassala dake gabashin kasar ta Sudan.

Bisa ga wannan umarnin, dokar ta-bacin zata shafe tsawon watannin 6 ne.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China