in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang ya tashi zuwa kasar Cambodia don halartar taron koli na biyu kan hadin gwiwar yankunan kogin Lancang da kogin Meigong
2018-01-10 11:14:02 cri
Da safiyar yau Laraba ne firaministan kasar Sin Li Keqiang ya tashi daga birnin Beijing zuwa Phnum Penh na kasar Cambodia, don halartar taron shugabanni karo na biyu, kan hadin gwiwar yankunan kogin Lancang da kogin Meigong tare da ziyartar kasar ta Cambodia.

Wannan ce ziyara ta farko da firaministan kasar Sin ya kai wata kasa ta waje a shekarar 2018. Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Kong Xuanyou ya bayyanawa 'yan jarida a kwanakin baya cewa, wannan ce ziyara ta farko da kasar Sin ta shirya gudanarwa a fannin diplomasiyya, wadda ke da babbar ma'ana ga hadin gwiwar yankunan kogin Lancang da kogin Meigong, kana za ta haifar da babban tasiri ga raya dangantakar dake tsakanin Sin da Cambodia a nan gaba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China