in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya gana da shugabannin kasashen tsakiya da gabashin Turai
2017-11-28 10:26:21 cri

Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya halarci taron ganawa karo na 6 da aka gudanar tsakanin shugabannin kasashe 16 na tsakiya da gabashin nahiyar Turai da kuma kasar Sin, jiya Litinin, a birnin Budapest na kasar Hungary.

A jawabin da ya yi ga taron, Mista Li ya ce, yadda ake samun ci gaba cikin sauri dangane da hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen tsakiya da gabashin Turai 16 gami da kasar Sin, ya sheda amfanin manufar da ake bi ta "zama cikin daidaituwa, da tattaunawa, da kokarin amfanawa juna, da bude kofa, da hakuri da bambancin ra'ayi, da kokarin kirkiro sabbin fasahohi", yayin da ake hadin gwiwar.

Firaministan kasar Sin ya kara da cewa, yayin taron wakilan jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 19 da ya gudana a watan jiya, an jaddada burin kasar Sin na neman samun ci gaba ta hanyar zaman lafiya, da kokarin kafa sabuwar dangantakar kasa da kasa, da samar da kyakkyawar makoma ta bai daya ga daukacin al'ummomin duniya.

A cewar jami'in, ana kokarin hadin gwiwa tsakanin kasashen dake yankin tsakiya da gabashin nahiyar Turai da kasar Sin ne ba domin takara da wasu kasashe na daban ba. Inda ya ce an yi haka ne don tabbatar da moriyar tattalin arziki, gami da raya huldar dake tsakanin bangarorin 2.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China