in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan kunan bakin wake ya hallaka mutane 10 a harin wani masallaci
2018-01-03 21:05:15 cri
Mutane 10 sun rasa rayukansu, sakamakon harin wani dan kunar bakin wake a garin Gamboru dake jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya.

Rahotanni daga jihar dai sun tabbatar da cewa, wani saurayi ne dauke da damarar ababen fashewa ya kutsa kai cikin masallacin dake garin na Gamboru, yayin sallar Asubar Larabar nan, ya kuma tada ababen fashewar dake jikin sa.

An ce cikin mutane 10 da suka rasu hadda mahaifin dan kunar bakin wajen. Tuni kuma aka garzaya da wadanda suka jikkata zuwa asibiti.

Wani mazaunin yankin da ya shaida aukuwar lamarin mai suna Abba Lawan, ya ce kafin aukuwar hakan, matashin dan kunar bakin waken ya kauracewa danginsa, ya koma daji inda 'yan ta'adda suke samun mafaka. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China