in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nijeriya ya yi tir da hare-haren da aka kai kasar yayin bikin sabuwar shekara
2018-01-03 10:30:12 cri
Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan hare-haren da ya kira na rashin hankali, da aka kai wasu yankunan kasar yayin bikin sabuwar shekara, al'amarin da ya yi sanadin asarar rayuka da jikkatar fararen hula.

Wata sanarwa da ta shiga hannun Kamfanin dillancin labarai na Xinhua ta ruwaito shugaba Buhari na bayyana al'amarin a matsayin wanda bai dace ba, da ba za a taba amincewa da shi ba.

Da safiyar ranar Litinin ne wasu 'yan bindiga suka farwa gida basaraken yankin Sanga na jihar Kaduna dake arewa maso tsakiyar kasar, inda suka kashe shi tare da matarsa. Haka zakila a ranar ne aka kai harin kan wasu mutane dake dawowa daga coci bayan gudanar da addu'ar shiga sabuwar shekara a jihar Rivers mai arzikin man fetur. Sannan kuma a jiya Talata a aka kai wasu hare-hare a yakunan Guma da Logo na jihar Benue. Hare-haren da suka yi sanadin mutuwa da jikkatar mutane da dama.

Muhammadu Buhari ya umarci hukumomin tsaro dake jihohin su kara matse kaimi a kokarin da suke don gaggauta tabbatar da maharan sun fuskanci fushin hukuma.

Shugaban ya kuma yi kira ga al'ummar yankunan da su guji daukar fansa, inda ya bukaci su ba hukumomin tsaro damar gudanar da bincike don tabbatar da hukunta wadanda ke da hannu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China