Mai magana da yawun 'yan sandan jahar Mukhtar Hussaini Aliyu, ya tabbatarwa 'yan jaridu faruwar lamarin, sannan daya daga cikin 'yayan basaraken ya samu raunuka, kuma an kone gidansa kurmus a lokacin harin.
Wannan shi ne hari na uku na baya bayan nan da aka kaddamar a kudancin Kaduna cikin mako guda.
Basaraken wanda sarkin gargagajiya ne mai daraja ta 2, ya gamu da ajalinsa ne a lokacin da ya tashi daga fadarsa dake Gwantu inda ya nufi kauyensu na Arak, da nufin halartar bikin sabuwar shekara tare da talakawansa, inda aka hallaka shi.
Kakakin 'yan sandan ya bukaci a kwantar da hankulla kasancewa jami'an hukumar na iya bakin kokarinsu domin gudanar da bincike kan lamarin.(Ahmad Fagam)