in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana goyon bayan matakan Iraki na tabbatar da zaman lafiya
2017-12-11 19:57:20 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana cewa, kasarsa tana goyon bayan matakan da mahukuntan kasar Iraki ke dauka na tabbatar da zaman lafiya da raya tattalin arzikin kasar.

Lu Kang wanda ya bayyana hakan yau yayin taron manema labarai a birnin Beijing, ya ce kasar Sin tana taya wa kasar Iraki murnar nasarar da ta samu a yakin da take yi da ayyukan ta'addanci. Yana mai cewa, hakan wata babbar nasara ce ga hadin gwiwar kasa da kasa kan yaki da ayyukan ta'addanci. Kasar Sin tana fatan kasar Iraki za ta cimma nasara a kokarin da take na tabbatar da zaman lafiya da bunkasuwar kasar nan da nan.

A ranar Asabar din da ta gabata ce firaministan Iraki Haider al-Abadi ya ayyana nasarar sake kwato daukacin yankunan kasar da dakarun kasar suka yi daga hannun mayakan kungiyar IS. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China