in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bunkasar tattalin arzikin kasar Sin zai kai 6.7% a bana
2018-01-02 10:27:09 cri
Cibiyar nazarin manufofin tattalin arzikin kasar Sin wato CASS a takaice, ta fitar da wani rahoto kan harkokin tattalin arziki, inda ta yi hasashen cewa, a shekarar da muke ciki, wato 2018, alkaluman GDP na kasar za su karu zuwa kashi 6.7 bisa dari.

Rahoton ya ce, a nan gaba, kasar Sin za ta kara nuna kwazo wajen aiwatar da manufofin kudi da na tattalin arziki gadan-gadan, kana, za ta yi iyakar kokarin shawo kan hadarurran da za su iya kunno kai da tallafawa mutanen dake fama da talauci da daidaita matsalar gurbacewar muhallin halittu da kuma yin kwaskwarima a wasu manyan fannoni. Rahoton ya yi imanin cewa, tattalin arzikin kasar Sin zai ci gaba da bunkasa da kyau kuma yadda ya kamata.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China