in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sudan ya sha alwashin karfafa rundunar tsaron kasarsa
2018-01-01 11:52:34 cri
Shugaba Omar Al-Bashir na Sudan, ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da daukar karin matakai na karfafa rundunar sojinta, ta yadda za ta iya tunkarar duk wata barazana daga masu nufin aikata muggan laifuka a kasar.

Shugaban wanda ya bayyana haka a jiya Lahadi, yayin bikin zagayowar shekaru 62 da samun 'yancin kan kasar, ya ce wannan aiki zai shafi duk wasu sassa na tabbatar da tsaro, da kandagarkin aukuwar laifuka, tare da tabbatar da an dakile masu fatan tarwatsa 'yancin kan kasar ko albarkatunta.

Shugaba Al-Bashir ya kara da cewa, duk wani yunkuri na samar da sulhu da hadin kan kasa ba zai yi tasiri ba, muddin aka gaza samar da managarcin tsaro.

Daga nan sai ya jaddada aniyarsa ta aiki tare da sauran kasashen duniya a fannin hadin gwiwa, domin cimma nasarar wanzar da zaman lafiya da tsaron yankuna, da kuma sassan kasa da kasa. Baya ga yunkurin dakile ayyukan kungiyoyin 'yan ta'adda da masu safarar kudade ko bil Adama. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China