Za a yi bikin daga tutar kasar Sin a ranar farko ta watan Janairun shekarar 2018 a Beijing
Da misalin karfe 8 saura minti 24 na safiyar ranar farko na watan Janairun shekarar 2018, za a yi bikin daga tutar kasar Sin a filin Tian Anmen dake tsakiyar birnin Beijing. Wannan ne karo na farko da kungiyar sojoji masu faretin maraba da baki da kungiyar kide-kide ta rundunar sojan kasar Sin za su sauke wannan nauyin dake bisa wuyansu cikin hadin gwiwa. A daidai lokacin, gidan rediyo kasar Sin CRI zai watsa labaru game da bikin ga masu sauraronmu dake duk fadin duniya da harsunan Sinanci da Turanci kai tsaye ta dukkan gidajen rediyoyi wadanda suke hadin gwiwa da CRI a duk fadin duniya. (Sanusi Chen)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku