in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gyaran fuska ga kundin tsarin mulki na kan gaba a ajandar taron JKS
2017-12-27 14:59:42 cri
Sashen siyasa na kwamitin kolin JKS, ya amince da sanya tattaunawa game da yiwuwar yiwa wasu sassa na kundin tsarin mulkin kasar Sin gyaran fuska, cikin manyan ajandojin da za ta tattauna, yayin cikakken zama karo na 2 na kwamitin kolin jam'iyyar na 19 dake tafe cikin watan Janairu mai zuwa.

Shugaba Xi Jinping, wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin koli na JKS, shi ne ya jagoranci taron sashen siyasar na ranar Larabar nan, taron da kuma mahalartansa suka saurari rahoton aiki, daga kwamitin ladaftarwa da sanya ido na kwamitin kolin, tare da tattaunawa game da alkiblar da jam'iyyar ta sanya gaba, game da yaki da cin hanci da rashawa a shekarar ta 2018 mai zuwa. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China