in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An daina jin duriyar tauraron dan-Adam na kasar Angola da Rasha ta harba sararin samaniya
2017-12-28 19:12:43 cri

Kamfanin kera roka da zirga-zirgar sararin samaniya na kasar Rasha mai suna Energia wanda ya yi nasarar harba tauraron dan-Adam na kasar Angola zuwa sararin samaniya, ya ce an daina jin duriyar tauraron dan-Adam din a halin yanzu.

A ranar Talatar da ta gabata ce aka yi nasara harba tauraon dan-Adan din, da nufin watsa shirye-shiryen talabijin a kasar, amma bayan wani lokaci, sai sadarwa da shi ta katse.

A ranar 28 ga watan Nuwamban wannan shekara ce, kasar Rasha ta harba wani roka mai dauke da taurarin dan-Adam 19, amma kuma aka daina jin duriyarsu jim kadan bayan tashinsu zuwa sararin samaniya.

Da farko dai, an tabbatar da cewa, bangaren rokar dake dauke da taurarin dan-Adan din ya fada cikin teku. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China