in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta tura tawagar sanya ido a zaben shugaban kasar Liberia
2017-12-26 19:04:39 cri

Shugaban hukumar zartarwar kungiyar tarayyar Afirka AU Moussa Faki Mahama ya amince da tura wata tawagar masu sanya ido a zaben shugabancin kasar Liberia da ake gudanarwa a yau, bayan da kotun kolin kasar ta jinkirta gudanarsa a kwanakin baya, sakamakon zargin aikata a zagayen farko na zaben.

Shugaban wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a yau Talata, ta bayyana cewa, tawagar wadda ta isa kasar ta Liberia tun a ranar 23 ga wannan wata, za ta kasance a kasar har zuwa ranar 31 ga wata.

'Yan takara biyu ne dai ke fafatawa a zaben, wato George Weah na jami'yyar CDC da kuma mataimakin shugaban kasar Joseph Boakai na jam'iyyar UP mai mulkin kasar.(Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China