in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsohon shugaban Ghana zai jagoranci wakilan ECOWAS da za su sa ido a babban zaben kasar Liberia
2017-10-06 12:29:52 cri
Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen Afrika ta Yamma ECOWAS, ta nada tsohon shugaban kasar Ghana John Mahama, a matsayin wanda zai jagoranci wakilanta da za su sa ido kan babban zaben Liberia da za a yi ranar 10 ga wata.

Wata sanarwa da kungiyar ta fitar jiya, ta ruwaito cewa an nada tsohon shugaban kasar ne bisa la'akari da irin rawar da ya taka lokacin da yake jagorantar shugabannin kasashe mambobin kungiyar, ta fuskar wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin da ma nahiyar baki daya.

Tsohon shugaban kasar na Ghana, ya kasance jagoran wakilan kungiyar kasashe renon Ingila ta Common Wealth, da suka sa ido kan zaben kasar Kenya da aka yi a watan Augustan da ya gabata, haka zalika, ya jagoranci wakilan ECOWAS da suka shiga tsakani yayin rikicin mika mulkin kasar Gambia a farkon shekarar nna. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China