in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban Afirka ta Kudu ya lashe zaben shugabancin jam'iyyar ANC mai mulki
2017-12-19 09:41:56 cri

Jiya Litinin ne, mataimakin shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya lashe zaben shugabancin jam'iyyar ANC mai mulkin kasar a yayin cikakken zaman taron wakilan jam'iyyar karo na 54.

A wannan rana, mahalarta taron suka zabi sabbin shugabannin jam'iyyar, baya ga Cyril Ramaphosa da aka zaba a matsayin shugaban jam'iyyar, an kuma zabi David Mabuza a matsayin mataimakin shugaban jam'iyyar, Gwede Mantashe a matsayin jagoran kasa, yayin da aka zabi Ace Magashule a matsayin babban sakatare.

Mr. Ramaphosa dai shi ne zai maye gurbin shugaban jam'iyyar ANC na yanzu Jacob Zuma, a sa'i daya kuma, Jacob Zuma zai ci gaba da kasancewa shugaban kasar har zuwa shekarar 2019, wato lokacin da za a gudanar da babban zaben shugaban kasar Afirka ta Kudu.

Cyril Ramaphosa mai shekaru 65 ya lashe zaben mataimakin shugaban jam'iyyar ANC a watan Disamba na shekarar 2012. A watan Mayu na shekarar 2014 kuma, aka zabe shi a matsayin mataimakin shugaban kasar Afirka ta Kudu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China