in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zuma: Har yanzu Afirka ta Kudu na fama da matsalar bambancin launin fata
2017-12-16 12:12:09 cri

Shugaba Jacob Zuma na kasar Afirka ta Kudu ya bayyana a jiya Jumma'a cewa, duk da cewa kasarsa ta rungumi akidar sasantawa da gina kasa tun a shekarar 1994, amma har yanzu kan al'ummar kasar a rabe yake a fannoni al'adu da bambancin launin fata.

Shugaba Zuma wanda ya bayyana hakan cikin wani sako da ya aikewa 'yan kasar albarkacin ranar sasantawa na kasa da ta fado a yau Asabar 16 ga watan Disamba, ya ce, yana da muhimmanci a gare mu baki daya mu kara hada kai mu yi aiki tare domin ci gaban kasarmu da wadanda muke zaune a cikinta.

Zuma ya kuma yi amfani da wannan dama wajen yin kira ga 'yan kasar, da su yi aiki tare a matsayinsu na 'yan kasa domin yayyata akidar sasantawa, zaman lafiya da hadin kan al'umma.

Taken bikin ranar ta bana dai shi ne " Shekarar Olibo Tambo gwarzon yaki da wariyar launin fata na kasar. Sasantawa ta hanyar farfado da tattalin arziki da jin dadin jama'a. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China