in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana maraba da rawar da MDD za ta taka wajen warware takaddamar nukiliyar zirin Koriya
2017-12-06 10:17:51 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Geng Shuang ya sanar da cewa, Sin tana maraba da irin rawar da MDD za ta taka wanda zai taimaka wajen warware batun takaddamar nukiliyar zirin Koriya.

A ranar Litinin MDD ta sanar da cewa, Jeffrey Feltman, jami'in dake kula da harkokin siyasa na ofishin sakatare janar na MDD, zai kai ziyarar aiki a Koriya ta arewa tsakanin ranakun Talata zuwa Juma'a.

Geng ya shedawa 'yan jaridu cewa, a ziyarar da Feltman ya kawo kwanan baya a kasar Sin, ya gana da mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Li Baodong, kuma manyan jami'an biyu sun yi musayar ra'ayoyi game da wasu muhimman batutuwa da suka shafi MDDr. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China