in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
FM: babu abun da zai sauya tsarin abota dake tsakanin kasar Sin da Zimbabwe
2017-11-17 10:51:11 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya ce duk da yanayin da ake ciki a Zimbabwe, tsarin abotar dake tsakaninta da kasar Sin ba zai sauya ba.

Yayin zantawa da manema labarai a jiya Alhamis, Geng Shuang ya ce suna kyautata fatan cewa, al'amura za su daidaita, sannan za a warware dukkan batutuwa cikin ruwan sanyi a kasar.

A ranar Laraba da ta gabata ne rundunar sojin kasar Zimbabwe ta sanar da karbe iko da gwamnatin kasar dake yankin kudancin Afrika, tare da yi wa shugaban kasar Robert Mugabe mai shekaru 93 da matarsa daurin talala tun da safiyar ranar.

Shugabannin rundunar sun bayyana ta gidan talabijin na kasar cewa, yunkurin nasu ba ya nufin juyin mulki, illa dai, suna farwa masu laifi dake zagaye da shugaban, inda suka ce Robert Mugabe da iyalansa na cikin koshin lafiya, suna masu bada tabbacin tsaronsa.

Da yake amsa tambaya game da jarin kasar Sin a Zimbabawe, Geng Shuang ya ce hadin gwiwa da amincin dake tsakanin kasashen biyu ta kunshi dukkan bangarori, kuma tana amfanar al'umomin kasashen. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China