Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya ce Sin na fatan ganin an warware takaddamar siyasa da ta kunno kai a Zimbabwe cikin lumana.
Yayin wani taron manema labarai da ya gudana a jiya Laraba, Mr. Geng ya amsa tambayar manema labarai game da halin da ake ciki a Zimbabwe, inda ya ce Sin na bibiyar halin da ake ciki a kasar sau da kafa.
Mr. Geng ya kara da cewa, wanzuwar zaman lafiya da lumana, tare da bunkasar ci gaba a Zimbabwe, ya dace da bukatun kasar, da ma makwaftanta dake yankin ta, kuma buri ne na sauran kasashen duniya kawayenta. (Saminu Hassan)