in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Lu Kang: Cimma moriya tare ne kashin bayan alakar Sin da Koriya ta kudu
2017-11-20 20:14:25 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya ce cimma moriyar juna ne kashin bayan kyakkyawar dangantaka dake tsakanin Sin da Koriya ta kudu.

Mr. Lu Kang na wannan tsokaci ne gabanin ziyarar aiki da ministan harkokin wajen Koriya ta kudu Kang Kyung-wha zai gudanar a nan kasar Sin, tsakanin ranekun 21 zuwa 23 na watan Nuwambar nan da muke ciki, inda ake fatan mahukuntan kasashen biyu za su tattauna da juna game da al'amura dake janyo hankulansu.

Kakakin ya kuma yi fatan ganin Koriya ta kudu ta kara azama, wajen bunkasa dangantakar kasashen biyu cikin lumana da wanzuwar ci gaba mai dorewa, domin a kai ga fadada hadin gwiwa, wanda zai amfani al'ummun kasashen biyu, tare da wanzar da zaman lafiya da daidaito, da ma ci gaba, da wadata a dukkanin yankin da suke. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China