in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
António Guterres na adawa da dukkan matakin da bangare daya tilo ya dauka na kawo barazana ga kokarin shimfida zaman lafiya a yankin Gabas ta tsakiya
2017-12-07 13:24:57 cri
A bangaren MDD, bayan da shugaba Trump na kasar Amurka ya bayyana kudurinsa game da batun birnin Kudus, nan take, Mr. António Guterres, babban sakataren MDD a jawabin da ya gabatar, ya nuna adawa da dukkan matakin da bangare daya tilo ya dauka na kawo barazana ga kokarin shimfida zaman lafiya a yankin Gabas ta tsakiya. Yana fatan bangarorin Palesdinu da Isra'ila za su gaggauta komawa kan teburin yin shawarwari. Mr. António Guterres ya ce, "Tun a kwanankin farko bayan da na kama aikin babban sakataren MDD, a kullum ina nuna adawa da dukkan matakan da bangare daya tilo ya dauka na kawo barazana ga kokarin shimfida zaman lafiya a tsakanin Palesdinu da Isra'ila. Dole ne bangarorin Palesdinu da Isra'ila su tabbatar da matsayin karshe na birnin Kudus ta hanyar yin shawarwari cikin lumana bisa kuduran da aka zartas a yayin tarukan kwamitin sulhu da na babban taro na MDD a lokacin da ake tattara ra'ayoyin daidaikun Palesdinu da Isra'ila."

A waje daya, Mr. António Guterres ya bayyana cewa, a matsayinsa na babban sakataren MDD, zai yi duk kokarin da ya dace na goyon bayan yin shawarwari mai ma'ana tsakanin shugabannin Palesdinu da Isra'ila domin cimma burin shimfida zaman lafiya a tsakaninsu har abada. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China