in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in MDD ya yi gargadi game da makomar ayyana Jerusalem a matsayin babban birnin Isra'ila
2017-12-06 10:11:35 cri
Sakatare janar na MDD Antonio Guterres, yana dakon sauraron sanarwar da shugaba Donald Trump na Amurka zai bayar na ayyana Jerusalem a matsayin babban birnin Isra'ila a hukumance, sai dai ya yi gargadi game da abin da ka iya biyowa bayan daukar wannan mataki.

A sanarwar da kakakin MDD Stephane Dujarric ya yi wa taron manema labarai a helkwatar MDDr dake birnin New York ya ce, mista Guterres ya sha yin gargadi kan daukar wannan mataki, wanda yake ganin lamari ne da zai iya gurgunta yunkurin warware takaddamar dake tsakanin sassan biyu.

A ranar Talata ne, shugaba Trump ya shedawa Isra'ila da shugabannin kasashen Larabawa cewa, ya daura aniyar dauke ofishin jakadancin Amurka a Isra'ila daga birnin Tel Aviv zuwa Jerusalem, matakin da ake ganin ka iya haifar da tashin hankali a yankin.

A yau Laraba ne kuwa, ake sa ran Trump zai bayyana matsayar da ya dauka kan wannan batu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China