in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun ko-ta-kwana na gabashin Afrika sun kammala rawar daji a Sudan
2017-12-04 10:37:14 cri
A ranar Lahadin da ta gabata dakarun tsaron ko-ta-kwana na gabashin Afrika (EASF) suka kammala shirin samun horo mai taken "Mashariki Salaam II," a sansanin horas da sojoji na Gebeit dake gabashin kasar Sudan.

Shirin rawar dajin ya samu halartar rundunonin soji daga kasashen Sudan, Somalia, Djibouti, Kenya, Uganda, Seychelles, Comoro Islands, Habasha, Rwanda da Burundi.

Ministan tsaron kasar Sudan Awad ibn Auf, wanda ya jagoranci bikin kammala taron ya bayyana cewa, dakarun na EASF a shirye suke su tunkari mayakan 'yan ta'adda dake zaune tsaye a wasu kasashen dake shiyyar.

Shugaban shirin EASF, Ambassador Issimail Chanfi, wanda ya gabatar da jawabi a lokacin bikin ya ce, shirin rawar dajin ya tabbatar da daga matsayin EASF na kasancewa kwararru, kuma a halin yanzu EASF tana da karfin da za ta iya tunkarar shirin wanzar da zaman lafiya a zahiri.

A shekarar 2004 ne aka kafa dakarun ko-ta-kwana na EASF a matsayin da ya daga cikin tawagogin dakarun wanzar da zaman lafiya biyar da ake da su a Afrika, kana an dora mata alhakin wanzar da zaman lafiya da tsaro a shiyyar gabashin Afrika. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China