in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 25 aka hallaka a wani sabon tashin hankali a arewacin Sudan ta kudu
2017-11-24 10:24:03 cri
Mahukunta a Sudan ta kudu sun sanar cewa, kimanin mutane 25 ne aka hallaka a wani sabon fada da ya barke tsakanin sojojin gwamnati da 'yan tawayen arewacin kasar a garin Leer.

Ministan yada labaran kasar mai kula da yankin kudancin jahar Liech Peter Makouth Malual ya bayyana cewa, fadan ya barke ne a farkon wannan mako tsakanin sojojin gwamnati da 'yan tawayen (SPLA-IO), wadanda ke biyayya ga tsohon mataimakin shugaban kasar Riek Machar, kuma an cigaba da gwabza fadan har zuwa ranar Laraba.

Malual ya ce, akalla 'yan tawaye 20 da kuma sojojin gwamnati 5 ne aka kashe a lokacin tashin hankalin. Sai dai ministan ya dora alhakin tayar da rikicin kan 'yan tawayen.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China