in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco zata karbi bakuncin taron dandali kan sha'anin tsaron Afrika
2017-09-19 10:13:16 cri
Birnin Casablanca na kasar Morocco zai karbi bakuncin sabon taron dandalin Afrika game da batun tsaro tsakanin ranakun 8 zuwa 10 ga watan Oktoba, jami'an shirya taron ne suka tabbatar da hakan a ranar Litinin.

Taron na 2017 zai samu halartar sama da wakilai 400 daga kasashen Afrika 45 domin tattauna batun hadin kan kasashen Afrika game da yaki da ta'addanci, da tsattsauran ra'ayi da aikata laifuka a kan iyakoki.

Shugaban dandalin Driss Benamer ya yi wa taron manema labarai karin haske game da manufar shirya taron. Ya ce taron zai mai da hankali ne kan manyan batutuwa 3 da suka hada da batun ta'addanci da yin kutse ta hanyar na'urorin zamani, da batun sabbin hanyoyin masu tsattsauran ra'ayi, da sabbin kalubalolin bakin haure da masu aikata laifuka a kan iyakokin kasashe da kuma duba batun hadin kai tsakanin kasashen Afrika da irin sabbin kalubalolin dake tattare da batun.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China