in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bakin haure 31 sun mutu a tekun yammacin Libya
2017-11-26 13:35:17 cri
Rundunar 'yan sandan dake tsaron bakin teku a karkashin rundunar sojan ruwan kasar Libya ta ce, an gano gawawwakin bakin haure kimanin 31 a tekun dake yammacin kasar, kana an yi nasarar kubutar da wasu bakin haure kimanin 500.

Abu-Ajela Ammar, shi ne kwamandan rundunar 'yan sanda masu tsaron bakin tekun ya bayyana cewa, lokacin da jami'an sintiri suka isa wurin, kwale-kwalen ya riga ya kife, inda aka gano gawawwaki da dama, tare kuma da wasu bakin hauren dake cikin ruwa, wadanda ba su da koshin lafiya. Bisa labarin da aka samu an ce, musabbabin kifewar kwale-kwalen shi ne, ya dauko fasinjoji fiye da kima.

Abu-Ajela Ammar ya kara da cewa, jami'an sintiri sun kara gano wani kwale-kwalen roba mai dauke da bakin haure guda 120, yayin da suka dauko bakin hauren da suka tsallake rijiya da baya zuwa sansanin sojan ruwa dake birnin Tripoli.

Tun daga shekara ta 2011 zuwa yanzu, halin da ake ciki a kasar Libya ya kara ta'azzara, inda gwamnatin kasar ba ta iya kulawa da bakin tekun kasar yadda ya kamata, lamarin da yasa wasu bakin hauren suka ratsa ta kasar Libya, suka tsallaka Bahar Rum har suka isa kasashen Turai. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China