in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yarjejeniyar warware rikicin siyasar Libya da MDD ke marawa baya na fuskantar matsala
2017-11-24 09:30:14 cri
Yarjejeniyar warware dambarwar siyasar kasar Libya dake samun goyon bayan MDD ya sake gamuwa da cikas, bayan da wani bangare ya yi watsi da shawarar da wakilin MDD dake kasar ya gabatar na yiwa yarjejeniyar gyaran fuska.

A kwanakin nan ne tawagar MDD dake kasar ta Libya ta shirya tattaunawa a kasar Tunsiya tsakanin wakilan jam'iyyun siyasar kasar ta Libya domin yiwa yarjejeniyar siyasar gyaran fuska, matakin farko da wakilin tawagar MDD dake Libya Ghassan Salame ya dauka a watan Satumban wannan shekara da nufin kawo karshen bambance-bambancen siyasar da kasar ke fuskanta.

A ranar Talatar da ta gabata ce majalisar dokoki dake gabashin kasar ta amince da shawarar da MDD ta gabatar na aiwatar da wannan gyara, sai dai kuma abokiyar adawarta ta yi watsi da wannan shawara, inda ta sanar da yiwuwar shirya zabuka cikin watanni shida domin kafa gwamnati mai kunshe da masana.

Masu sharhi na cewa, wannan mataki tamkar mayar da hannu agogo baya ne, a kokarin da ake na kawo karshen dambarwar siyasar kasar, lamarin da ka iya kaiwa ga samun gwamnati ta uku, bayan biyun da ake da su yanzu haka.

Kasar Libya dai ta tsunduma cikin rikicin siyasa ne, tun bayan boren shekarar 2011 wanda ya kai ga hambarar da gwamnatin marigayi Gaddafi, lamarin da ya haifar da rudani da matsalar tsaro a kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China