in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba da firaministan Sin sun mika sakon jaje ga takwarorinsu na Masar
2017-11-25 17:14:40 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika sakon ta'aziyya ga takwaransa na kasar Masar Abdel Fattah al Sisi a yau Asabar, inda ya nuna juyayi game da harin ta'addanci da aka kai wa kasar, tare kuma da yi wa iyalan wadanda suka rasa rayukansu ta'aziyya.

Haka kuma, Xi Jinping ya ce, kasar Sin tana adawa da dukkan nau'ikan ta'addanci, tana kuma yin Allah wadai da harin da aka kai wa kasar, yana mai cewa, Sin za ta kuma goyi bayan kasar Masar wajen kiyaye zaman lafiya da yaki da 'yan ta'adda.

Haka zalika, Firaministan kasar Sin Li Keqiang, shi ma ya mika sakon jaje ga takwaransa na Masar Sherif Ismail, inda ya jajantawa iyalan wadanda suka rasu da kuma wadanda suka jikkata.

Mr. Li ya ce, kasar Sin za ta hada hannu da kasar Masar wajen yaki da ta'addanci. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China