in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta bayyana damuwa kan kasonta na Kogin Nile bayan taron da ta yi da Habasha da Sudan ya gaza cimma nasara
2017-11-13 09:18:08 cri
Kasar Masar ta bayyana damuwa game da kasonta na ruwan Kogin Nile bayan taron da ta yi da kasashen Habasha da Sudan ya gaza amincewa da wani rahoto kan tasirin sabuwar madatsar ruwan Habasha a kan kasashen.

Taron yini biyu na kwamitin kwararrun kasashen Masar da Habasha da Sudan kan madatsar ruwan Habasha ta GERD da aka fara a ranar Asabar, ya gaza amincewa da wani rahoton bayani da wani kamfanin tuntuba ya yi game da tasirin Madatsar kan kasashen Sudan da Masar.

Ministan albarkatun ruwa da noman rani na Masar Mohammed Abdel-Aati, ya ce kasarsa ta damu da rashin nasarar taron wanda zai kawo tsaiko ga nazarin na kwararru, duk da kokarin kasarsa cikin watannin da suka gabata na tabbatar da an kammala nazarin cikin lokaci.

Ministocin Habasha da Sudan sun ki amincewa da rahoton kamfanin tuntubar, duk da amincewa da shi da Masar ta yi tun da farko, inda suka nemi wasu gyare-gyare da za su shafi rahoton tare da mayar da shi maras ma'ana.

Masar ta damu ne da kasonta na kubik mita biliyan 55.5 na ruwan Kogin Nile yayin da ake tsaka da ginin madatar ruwan GERD. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China