Kafin wannan, jam'iyyar ZANU-PF ta gudanar da taron kwamitin kolin na jam'iyyar na musamman, inda aka kori Mugabe daga shugabancin jam'iyyar kana babban sakataren jam'iyyar. Kana aka tsaida kudurin mayar da tsohon mataimakin shugaban kasar Emmerson Mnangagwa a matsayin memban jam'iyyar aka kuma nada shi a matsayin shugaban jam'iyyar kuma babban sakatarenta.
A jawabinsa, Mugabe ya ce, bai amince da kudurorin da jam'iyyar ta tsaida a wannan rana ba.
Ya ce, ya kamata a canja mukamin shugaban jam'iyyar bisa oda. Ana fatan warware matsalar a yayin taron wakilan jam'iyyar ZANU-PF da zai shugabanta a watan Disamba mai zuwa. (Zainab)