in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta karfafa matakan kare 'yancin mallakar fasaha
2017-11-23 10:23:42 cri
Kasar Sin ta bayyana kudurinta na kare 'yancin mallakar fasaha, a wani mataki na inganta matakan raya tattalin arzikin kasar. Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da aka fitar bayan kammala taron majalisar gudanarwar kasar da firaminista Li Keqiang ya jagoranta jiya Laraba.

Sanarwar ta kara da cewa, daga yanzu za a kara samar da kariya kan yadda ake gudanar da harkokin kasuwanci da ma 'yancinsu na mallakar fasaha, kana a hannu guda su ma kamfanoni masu zaman kansu za su ci gajiyar da kamfanonin gwamnatin ke samu na kariyar 'yancin mallakar fahasa.

Haka kuma sanarwar ta ce, za a kara kare 'yancin mallakar fasaha na kayayyakin cikin gida, za kuma a rika a daidaita laifukan da suka shafi tattalin arziki kamar yadda dokoki suka tanada.

Idan ba a manta ba, muhimmin rahoton da aka gabatarwa taron wakilan JKS karo na 19, ya bayyana cewa, wajibi ne gyare-gyaren da ake aiwatarwa a fannin tattalin arziki ya mayar da hankali kan inganta tsarin kare 'yancin mallakar fasaha da tabbatar da a sakarwa kasuwa mara game da yadda za a rika samar da kayayyaki.

Rahoton aikin gwamnati na wannan shekara, ya bayyana cewa, kare 'yancin mallakar fasaha na nufin kare 'yan kwadago, kirkire-kirkire, da karewa da kuma samar da tsarin ma'aikata masu inganci.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China