in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi ya mika sakon ta'aziyyar mummunan harin bom da ya kashe mutane a Somaliya
2017-10-18 10:39:10 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sakon ta'aziyya ga takwaransa na kasar Somaliya, Mohamed Abdullahi Mohamed, sakamakon mummunan harin bom wanda ya hallaka daruruwan mutane a Mogadishu, babban birnin kasar Somaliya.

A sakon ta'aziyyar, Xi ya ce, ya yi matukar kaduwa da samun labarin mummunan harin wanda ya hallaka mutane masu yawa.

A madadin gwamnati da jama'ar kasar Sin da kuma shi kansa shugaba Xi, yana nuna juyayi game da hasarar rayukan da aka samu a kasar Somaliya, kana yana jajantawa iyalan wadanda harin ya rutsa da su, da kuma fatan samun sauki cikin hanzari ga wadanda suka jikkata a harin.

A kalla mutane 276 ne harin ya hallaka, wasu mutanen sama da 300 kuma sauka jikkata a harin bom din wanda ya faru a ranar Asabar a wasu rukunin shaguna a Mogadishu, an bayyana harin da cewa shi ne mafi muni da aka taba samu a tarihin hare-haren da ake kaddamarwa a kasar ta Somaliya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China