in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya zanta da sarkin Saudiyya ta waya
2017-11-17 10:29:38 cri
Jiya Alhamis, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya zanta da sarkin kasar Saudiyya, Salman bin Abdulaziz Al Saud ta waya.

Yayin tattaunawar tasu, Sarki Salman ya taya Xi Jinping murnar sake zama babban sakatare na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, da rufe babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar karo na 19 cikin nasara, inda ya kuma ya jaddada cewa, babu tantama babban taron zai jagoranci al'ummar kasar Sin wajen samun nasara.

Salman ya kuma ce, alakar dake tsakanin Saudiyya da Sin na samun babban ci gaba, kuma kasarsa na fatan fadada hadin-gwiwa tare da Sin, musamman ma a fannonin da suka shafi makamashi, da harkokin kudi. Kaza lika Saudiyya na fatan zama babbar aminiyar kasar Sin a yankin Gulf, da dukufa ka'in da na'in, kan zurfafa dangantakar abokantaka ta hadin-gwiwa bisa manyan tsare-tsare tare da kasar Sin, al'amarin da zai taimaka ga tabbatar da zaman lafiya, da kwanciyar hankali a duk fadin duniya.

A nasa bangaren kuma, shugaba Xi Jinping ya ce, Sin da Saudiyya aminan juna ne, wadanda ke kara samun amincewa da hadin-gwiwa tsakaninsu. Har ila yau kasar Sin na fatan ci gaba da kokari tare da Saudiyya, domin kara aiwatar da shawarar 'ziri daya da hanya daya', da habaka hadin-gwiwa daga fannoni daban-daban. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China