in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana sa ran Nijeriya za ta rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da Boeing wajen samar da jirgin saman kasar
2017-11-17 09:46:49 cri
Gwamnatin Nijeriya ta sanar da shirinta na rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna tsakaninta da kamfanin Boeing wajen kafa kamfanin jirgin saman kasar.

Karamin ministan kula da sufurin jiragen saman kasar Hadi Sirika da ya bayyana haka a jiya, ya ce za a sa hannu kan yarjejeniyar ne a cikin mako mai zuwa a Abuja, babban birnin kasar.

Hadi Sirika, ya ce kamfanin Airbus na kasar Fransa ma ya nuna sha'awarsa na hadda hannu da gwamnatin Nijeriya wajen kafa kamfanin kula da yin gyara da kuma yi wa jiragen sama garambawul a kasar.

Ministan ya ce kudurin gwamnatin na kafa kamfanin jiragen sama da na kula da gyara jiragen, yunkuri ne na sake fasalin bangaren sufurin jiragen saman.

Tuni gwamnatin ta sanar da nada masu bada shawarwari game da kafa kamfanonin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China