in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nigeria na aiki tukuru wajen magance radadin matsin tattalin arziki
2017-11-17 09:31:38 cri
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya ce kasar na shawo kan matsin tattalin arziki, kuma kokarin da gwmanatinsa ke yi na da nufin saukaka radadin matsin ta hanyar samar da karin ayyukan yi da tallafawa iyalai masu rauni da magance rashin aikin yi da kuma samar da ababen more rayuwa.

Da yake jawabi yayin kaddamar da wani littafi a Abuja, babban birnin kasar a jiya Alhamis, Muhammadu Buhari ya ce, yana son ya ba al'ummar kasar tabbacin kudurinsa na inganta tsaro da yaki da cin hanci da sake fasalin tsarin tattalin arziki.

Gwamnatin Buhari dai na daidai tsakiyar wa'adinta, inda littafin mai shafuka 360 ya tabo nasarori da gwamnatin ta samu a fannonin siyasa da zaman takewa da ci gaban tattalin arziki.

Muhammadu Buhari, ya shaidawa mahalarta taron cewa, yakin da ake da cin hanci ya fara samun kyawawan sakamako.

Har ila yau, ya ce kasar za ta iya biyan basusukan da ake binta. Yana mai cewa, darajar takardar lamunin kasar na kasashen waje ya zarce kima.

Shugaban ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da kokarin magance rikicin makiyaya da manoma da yaki ci yaki cinyewa da matsalar satar mutane dan neman kudin fansa da kuma fashi da makami. (Fa'iza Musatpha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China