in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guterres: Sin na mai da hankali matuka ga yaki da ta'addanci
2017-11-17 09:12:21 cri
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya jinjinawa kasar Sin, bisa abun da ya kira kwazonta na tallafawa yaki da ayyukan ta'addanci a mataki na kasa da kasa.

Da yake amsa tambayoyin wakilin kamfanin dillancin labarai na Xinhua, bayan gabatar da wata makala game da yaki da ta'addanci, da kare hakkokin bil'adama a jami'ar London, Mr. Guterres ya bukaci Sin ta ci gaba da wannan muhimmin aiki da take gudanarwa. Ya ce akwai matukar bukatar kasashen duniya su dage, wajen hadin gwiwa da juna a fannin yaki da ta'addanci, wanda a cewarsa muhimmancin hakan ya sa a badi, zai kira taron shugabannin hukumomin yaki da ayyukan ta'addanci irinsa na farko karkashin inuwar MDD, domin fadada hadin kai wajen gina tsari, na tallafawa juna da amincewa juna a fannin.

Babban magatakardar MDDr ya kuma bukaci kasashe mambobin majalissar, da su himmatu wajen ganin sun dakike hanyoyin da 'yan ta'adda ke bi, wajen samarwa kungiyoyin su kudade, da bunkasa musaya a fannin tsaro.

Ya ce a shekarar da ta gabata kadai, an samu aukuwar hare-haren ta'addanci har 11,000 a kasashe sama da 100. Yana mai kashedin cewa hakan barazana ce ga zaman lafiya, da tsaro, da ma ci gaban daukacin kasashen duniya. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China