in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afirka ta kudu ta bukaci a warware takaddamar siyasa a Zimbabwe cikin ruwan sanyi
2017-11-16 10:29:49 cri
Shugaban kasar Afirka ta kudu Jacob Zuma, ya nuna damuwa game da halin rashin tabbas da kasar Zimbabwe ke fuskanta, yana mai kira ga daukacin masu ruwa da tsaki, da su kawo karshen hakan cikin lumana.

Shugaba Zuma ya ce akwai bukatar rundunar sojojin Zimbabwe ta dauki matakai na lumana, wajen warware takaddamar siyasa da ta dabaibaye kasar, sai dai a cewarsa ya dace dukkanin matakan da za a dauka su kasance na lumana, ba kuma wadanda za su haifar da illa ga harkokin tsaron kasar ba.

Ya ce kungiyar bunkasa yankin kudancin Afirka ta SADC, za ta ci gaba da sanya ido kan halin da ake ciki a Zimbabwe, za kuma ta bada taimako a duk lokacin da bukatar hakan ta taso, kamar yadda hakan ke cikin kudurorin kafa ta.

Yanzu haka dai Afirka ta kudun ce ke jagorancin kungiyar ta SADC. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China