A safiyar Larabar hafsoshin sojin kasar Zimbabwe sun bada sanarwa ta gidan talabijin din kasar cewa, ba su kwace ikon gwamnatin kasar ba, amma suna yunkurin zakulo wasu masu laifi ne dake kewaye da gwamnatin shugaba Robert Mugabe na kasar.
A jawabin da manyan jami'an sojin kasar suka watsa kai tsaye ta gidan talabijin na kasar sun ayyana cewa, shugaba Mugabe da iyalansa suna cikin tsaro da kwanciyar hankali, kuma dakarun sojin suna ci gaba da gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. (Ahmad Fagam)