Shugaba Buhari ya yi wannan kira ne a jiya Laraba cikin wata sanarwa da fadar gwamnatinsa ta fitar, yana mai jan hankalin shugabannin siyasa da tsagin rundunar sojin Zimbabwe, da su kaucewa daukar matakai da ka iya jefa kasar cikin mummunan yanayi maras dalili.
Ya ce kamata ya yi a dauki dukkanin matakai na warware takaddamar da sassan kasar ke fuskanta ta hanyar martaba kundin tsarin mulkin kasar, domin ta haka ne kawai za a kaucewa jefa kasar cikin halin ha'ula'i, wanda kuma ka iya shafar sauran kasashe dake yankin. (Saminu Hassan)