in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta bukaci Zimbabwe da ta dauki matakan warware tataburzar siyasa bisa doka
2017-11-16 09:47:01 cri
Kungiyar hadin kan Afirka ta AU, ta yi kira ga masu ruwa da tsaki a dambarwar siyasar da ta bullo a kasar Zimbabwe, da su dukufa wajen warware halin da kasar ke ciki yanzu haka, ta hanyar biyayya ga tanaje tanajen kundin tsarin mulkin kasar.

Shugaban hukumar zartaswar kungiyar ta AU Moussa Faki Mahamat, shi ne ya yi wannan kira a jiya Laraba, yana mai cewa kungiyar na bibiyar halin da ake ciki a Zimbabwe, bayan da sojoji suka amshe iko a jiya.

Mr. Mahamat ya ce "Ina kira ga dukkanin masu ruwa da tsaki, da su dauki matakan warware sabani ta hanyar martaba dokokin kundin tsarin mulkin kasar, da ma sauran tanaje tanaje na kungiyar ta AU, ciki hadda sashen da ya ayyana bukatar martaba mulkin dimokaradiyya na nahiyar Afirka, da harkar zabe, tare da gudanar da sahihiyar gwamnati. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China