in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Mugabe na Zimbabwe ya kori mataimakinsa
2017-11-07 09:21:54 cri
Shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe, ya kori mataimakinsa Emmerson Mnangagwa, inda ya zarge shi da rashin biyayya da kuma gazawa wajen tafiyar da aikinsa.

Ministan yada labaran kasar Simon Khaya Moyo, ya shedawa taron manema labarai a babban birnin kasar cewa, korar ta mista Emmerson ta fara aiki ne nan take.

Moyo ya ce, bisa dokar kundin tsarin mulkin kasar Zimbabwe, shugaba Robert Mugabe ya tube mataimakinsa Emmerson Mnangagwa daga kan mukaminsa na mataimakin shugaban kasar nan take.

Ya ce ta bayyana karara cewa mataimakin shugaban kasar ba ya gudanar da ayyukan dake wuyansa yadda ya kamata. Kana a koda yaushe yana nuna halin rashin da'a, da rashin girmamawa, da yaudara, da kuma rashin tabbas. Sannan yana nuna rashin gashiya wajen tafiyar da ayyukansa.

Mugabe ya nada Mnangagwa a matsayin mataimakinsa ne a shekarar 2014, bayan da ya sallami tsahon mataimakinsa Joice Mujuru bisa zarginsa da yunkurin haifar da baraka da kuma kokarin yi masa juyin mulki. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China