in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mugabe ya rantsar da sabbin ministocin da ya nada
2017-10-11 10:14:57 cri
A jiya Talata ne shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe, ya rantsar da sabbin ministocinsa 6 da ya nada bayan da ya yi garambawul a majalisar ministocin kasar a ranar Litinin da ta gabata.

Biyu daga cikin sabbin ministocin ba su halarci wajen ba, amma ana sa ran rantsar da su a wani lokaci nan gaba.

Ministocin da suka sha rantsuwar kama aikin su ne tsohon shugaban hukumar tattara bayanan sirri Happyton Bonyongwe, wanda aka nada a matsayin ministan shara'a, wanda ya karbi aiki daga hannun mataimakin shugaban kasar Emmerson Mnangagwa, sauran su ne ministan ci gaban matasa, da ministan hukumar kula da 'yan kasa da samar da ayyukan yi Chiratidzo Mabuwa, da Edger Mbwembwe, a matsayin sabon ministan yawon bude ido.

Mabuwa shi ne tsohon mataimakin ministan ciniki da masana'antu, yayin da Mbwembwe ya kasance mataimakin ministan harkokin waje.

Gyaran fuskar da shugaba Mugabe ya yi wa majalisar ministocin kasar ya shafi ministoci 10 ne, inda ya nada sabbin ministoci 8 kana ya sauke ministoci 3. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China