in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Miliyoyin mutane na cikin hadari yayin da aka shiga mako na biyu da rufe iyakokin kasar Yemen
2017-11-15 11:23:55 cri
Babban jami'in hukumar bada agaji ta MDD a Yemen Jamie McGoldrick, ya yi gargadin cewa, dubban mutane na cikin matsanancin hadari, yayin da al'amura ke kara tabarbarewa, saboda rufe iyakokin kasar da kasa da na ruwa da na sama da aka yi.

Jamie McGoldrick ya bayyana a jiya cewa, akwai mutane miliyan 21 dake neman agaji, kuma miliyan 7 daga cikinsu, na cikin halin yunwa inda suka dogara kacokan a kan tallafin abinci.

Ya bayyana haka ne ga MDD ta wayar tarho, daga Amman na Jordan, saboda toshe hanyar isa Sanaa, babban birnin Yemen da aka yi.

Ya ce ci gaba da rufe tashoshin ruwa da na jiragen sama da rundunar kawancen da Saudi ke jagoranta ta yi, zai kara ta'azzara matsanancin halin da ake ciki. Yana mai cewa a ganinsa, matakin na barazana ne ga rayukan miliyoyin mutane dake kokarin rayuwa.

Ya kuma jadadda jawaban manyan jami'an MDD dake cewa, rikicin Yemen da aka fara watan Maris na 2015, ya haifar da matsalar jin kai mafi muni a duniya.

Ita ma hukumar UNHCR mai kula da 'yan gudun hijira ta MDD, ta ce ta kadu da yanayin jin kai da ke kara lalacewa a Yemen. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China